in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Mugabe na Zimbabwe ya yiwa majalisar ministocin kasar garan bawul
2017-10-10 11:05:15 cri
A ranar Litinin shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe, ya yi wa majalisar ministocin kasar gyaran fuska, kuma ya sauke mataimakinsa Emmerson Mnangagwa daga mukamin ministan shari'a na kasar yayin da ya sake mayar da ministan kudin kasar Patrick Chinamasa zuwa sabuwar ma'aikatar tsaron yana gizo da dakile barazanar yin kutse ta kasar.

Kafin yin garam-bawul din, Mnangagwa shi ne ke rike da mataimakin Mugabe a shugabancin jam'iyyar ZANU-PF mai mulkin kasar, kuma shi ne mataimakin shugaban kasar, kana ministan shari'a na kasar.

Tsohon ministan harkokin cikin gidan kasar Ignatius Chombo shi ne aka baiwa mukamin ministan kudin kasar, yayin da babban jami'in hukumar leken asirin kasar Happyton Bonyongwe shi ne aka nada a matsayin sabon ministan shari'a na kasar.

Tsohon ministan tsara tattalin arzikin kasar Obert Mpofu shi ne sabon ministan harkokin cikin gidan kasar, yayin da Patrick Zhuwao, baffa ne ga Mugabe wanda a baya yake rike da mukamin ministan matasa na kasar yanzu ya koma sabon ministan kula da ayyukan gwamnati da walwalar al'umma.

Garam bawul ga majalisar ministocin Zimbabwe ya zo ne a yayin da ake jajiberin zaben shugaban kasar, wanda za'a gudanar a shekarar 2018, inda shugaba Mugaben zai sake tsayawa takara a zaben. A shekarar 2015 ne Mugabe ya gudanar da gyaran fuska ga majalisar ministocinsa na karshe. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China