in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zimbabwe ya bukaci dunkulewar kasashen duniya don warware matsalolin dake addabar duniyar
2017-09-22 09:09:35 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Robert Gabriel Mugabe, yayi kira ga kasashen duniya da su kara hada kai da juna da yin aiki tare don samun nasarar cimma muradin ajandar samar da dawwamamman cigaban duniya nan da shekarar 2030.

Mugabe ya bayyana hakan ne a babban taron MDD inda ya bayyana halin da ake ciki game da cigaban kasashen duniya da cewa ya sha banban ta fuskoki da dama musamman idan aka yi la'akari da yadda wasu ke kallon cigaban duniya a matsayin buri, juyin-juya-hali, sauya fasali, gama-gari, wanda ya shafi dukkannin fannonin rayuwar bil adama.

Wannan ne dalilin da yasa ajandar ke bukatar hada karfi da karfe da dunkulewa waje guda, da yin aikin tare da kuma hadin kai, inji mista Mugabe.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China