in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya bukaci daukar matakan kara inganta huldar kasashen gabashin Asiya
2017-11-15 09:19:57 cri
Firaministan Sin Li Keqiang, ya bukaci daukar matakan bude sabon babi, na inganta huldar kasashen dake yankin gabashin Asiya. Mr. Li wanda ya bayyana hakan cikin jawabinsa, yayin taro karo na 12 na kasashen wannan yanki da ya gudana a birnin Manila na kasar Philippine, ya zayyana bukatar karfafa tattalin arzikin yankin, yana mai cewa zaman lafiya da samar da daidaito na kan gaba, cikin muhimman batutuwa da ake fatan cimmawa a wannan lokaci.

Firaministan na Sin ya ce kawo yanzu, ba a kai ga warware matsalolin da tattalin arzikin duniya ke fuskanta ba, baya ga kalubalen da rashin tabbas a fannin ke haifarwa, akwai kuma batutuwa na tsaron yankuna, ciki hadda barazanar ta'addanci dake kara bazuwa.

Ya ce a irin wannan yanayi, abu ne mai wahala a cimma daidaito, da wadatar tattalin arziki ko dunkulewar yankin gabashin Asiya wuri guda, don haka ya zama wajibi a yabawa dukkanin ci gaba da aka samu ko min kankantarsa.

Da ya tabo batun nasarar kammalar taron wakilan JKS karo na 19 da aka gudanar cikin watan jiya a nan birnin Beijing, Mr. Li ya ce taron ya amince da ci gaba da bin hanyoyin lumana wajen samar da ci gaba, da dada sabunta alakar kasa da kasa tsakanin Sin da sauran kasashen duniya, tare da gina al'ummar duniya dake da burin cimma moriyar juna.

Ya ce ci gaban kasar Sin zai haifar da damammaki na bunkasar kasashen dake yankin na gabashin Asiya, da ma sauran sassa na duniya baki daya, ba kuma zai haifar da wata barazana ga wani bangare ba. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China