in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da Kungiyar ASEAN za su samar da burin da dangantakarsu ke son cimmawa kawo shekarar 2030
2017-11-14 10:25:18 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya ce kasar Sin na neman a fitar da burin da ake son cimmawa zuwa 2030, daga hadin gwiwarta da kungiyar kasashen kudu maso gabashin Asiya, domin daukaka dangantakarsu.

Da yake jagorantar taron kasar Sin da kungiyar ASEAN karo na 20 a Manila tare da Shugabn Philippine Rodrigo Duterte, Li Keqiang ya ce burin zai daukaka tsare-tsaren hadin gwiwar kasar Sin da ASEAN zuwa wani sabon mataki ta yadda dangantakar za ta taba kowanne bangare yayin da za ta maida hankali ga batutuwa 3 da suka hada da tabbatar tsarin siyasa da tattalin arziki da cinikayya da kuma musaya tsakanin al'ummominsu.

Li Keqiang ya ce har kullum, kasar Sin na ba dangantakarta da ASEAN muhimmanci a harkar diflomasiyyar makotaka, kuma kudurinta ne daukar ASEAN a matsayin aminiya kuma makociya ta kwarai, da za su yi aiki tare wajen shawo kan kalubale da kuma samar da al'umma mai kyakkyawar mako da akidu da manufofi na bai daya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China