in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An zartas da sanarwar kwarya-kwaryan taron shugabannin kasashe membobin kungiyar APEC karo na 25
2017-11-12 13:19:37 cri
An rufe kwarya-kwaryan taron shugabannin kasashe membobin kungiyar APEC karo na 25 a birnin Da Nang dake kasar Vietnam a jiya ranar 11 ga wata, inda aka zartas da sanarwa tare da yin kira ga membobin kungiyar da su nuna goyon baya ga tsarin yin ciniki a tsakanin bangarori daban daban.

Shugaban kwarya-kwaryan taron a wannan karo kuma shugaban kasar Vietnam Tran Dai Quang, ya bayyanawa 'yan jarida bayan rufe taron cewa, an amince da kara yin mu'amala da juna a wannan yanki, da sa kaimi ga maida yankin a matsayin muhimmin yanki na hadin gwiwar tattalin arzikin duniya, da sa kaimi ga kafa yankin ciniki cikin 'yanci a wannan yanki.

Sanarwar da aka zartas a gun taron ta ce, shugabannin kasashe membobin kungiyar APEC suna son daukar matakai masu dorewa tare, da kara inganta hadin gwiwar dake tsakanin membobin kungiyar APEC, da sa kaimi ga samun bunksuwa mai dorewa ba tare da yin la'akari da bambance-bambance ba, da zurfafa tsarin bai daya na tattalin arziki a yankin, da nuna goyon baya ga hukumomin cinikayya da kamfanonin kanana da matsagaita, da kuma kara tabbatar da tsaron hatsi da raya aikin gona mai dorewa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China