in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya halarci taron kolin shugabannin masana'antu da kasuwanci na kungiyar APEC
2017-11-11 13:29:59 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron kolin shugabannin masana'antu da kasuwanci na kungiyar hadin gwiwar tattalin arzikin kasashen yankin Asiya da Pasifik wato APEC, da aka yi a birnin Da Nang na kasar Vietnam Jiya Jumma'a da yamma.

Yayin taron, Xi Jinping ya yi jawabi mai taken "yin amfani da damar kwaskwarima ta fuskar tattalin arzikin a kasashen duniya, wajen neman ci gaban yankin Asiya da Pasifik baki daya".

Wannan shi ne karon farko da shugaba Xi ya yi jawabi ga wani taron kasa da kasa tun bayan kammala taron wakilan JKS karo na 19.

Cikin jawabinsa, shugaban ya bayyana manufofin kasar Sin wajen neman ci gaban yankin Asiya da Pasifik cikin hadin gwiwa a wani sabon zamani na gaba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China