in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin mika tallafin shinkafa ga Zimbabwe
2017-09-12 11:20:45 cri

Kasar Sin ta mika tallafin shinkafa ga kasar Zimbabwe, inda aka gudanar da bikin mika tallafin a jiya Litinin, a Harare, fadar mulkin kasar.

Yayin bikin, Madam Prisca Mupfumira, Ministar kasar Zimbabwe mai kula da ayyukan kwadago da harkokin al'umma, ta godewa gwamnatin kasar Sin bisa tallafin da ta bayar.

A cewarta, yayin da ake raba tallafin, za a mai da hankali ga mutane masu rauni, musamman ma tsoffafi da nakasassu da marayu da mutanen da ambaliyar ruwa da sauran iftila'i suka ritsa da su

A nasa bangaren, jakadan kasar Sin dake Zimbabwe mista Huang Ping, ya ce kasarsa ta bayar da tallafin ne don cika alkawrin da shugaba Xi Jinping ya dauka yayin da ya ziyarci Zimbabwe, gami da halartar taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da ya gudana a birnin Johannesburg a karshen shekarar 2015.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China