in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane sama da miliyan 6 na fuskantar barazanar boma-bomai a kasar Sudan ta kudu
2017-11-05 13:01:16 cri
Ofishin kula da aikin haka nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa na MDD ya bayar da sanarwa a jiya Asabar cewa, akwai mutane sama da miliyan 6 a kasar Sudan ta kudu da ke zama a yankunan da ke fuskantar barazanar fashewar nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa, da kuma sauran boma-boman sakamakon yakin da aka fuskanta.

Sanarwar ta ce, ana iya gano boma-bomai da matsakaicin yawansu ya kai 150 a ko wane wata a kasar. Wadannan boma-bomai ba kawai sun hana fararen hula tserewa daga yankunan da ake fama da rikici ba, har ma sun kawo cikas ga taimakon jin kai, tare kuma da hana ci gaban tattalin arziki da al'ummar kasar baki daya.

Baya ga haka, sanarwar ta ce, ofishin na kokarin aikin bincike da kawar da boma-boman sakamakon yaki da kasar ta Sudan ta kudu ta fuskanta, da nufin ba da tabbacin tsaro ga masu aikin kiyaye zaman lafiya, kana da samar da yanayi mai kyau wajen gudanar da taimakon jin kai da farfado da yanayin zamantakewar rayuwar yau da kullum na 'yan kasar. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China