in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta Kudu ta nemi a kyautata zaman lafiya ta hanyar ayyukan raya kasa
2017-09-24 13:53:55 cri
A lokacin da yake kaddamar da jawabi a babban taron MDD, mataimakin shugaban kasa na farko na Sudan ta kudu ya bukaci a kyautata zaman lafiya da kwanciyar hankali ta hanyar mayar da hankali kan ayyukan raya cigaba da ayyukan gina al'umma na dogon lokaci.

Yace kasar Sudan ta kudu zata ninka kokarinta wajen inganta hanyoyin shigar da kayayyakin jin kan al'umma, ya kara da cewa, kasarsa tana fatan kasa da kasa zasu kara azama wajen samar da cigaba da kuma ayyukan jin kai a kasar ta Sudan ta kudu.

Yace babban abin dubawa shine yadda Sudan ta kudun zata samu damammaki wadanda zasu taimaka wajen wanzar da zaman lafiyar al'ummar kasar baki daya, da kuma yadda zasu samu damar zabar shugaban da suke son ya jagorance su ta hanyar karbabbe kuma sahihin zabe.

Yace kasar ta fuskanci dubun dubatar 'yan gudun hijira da wadanda rikici ya raba su da matsugunansu, amma sannu a hankali suna komawa gidajensu bisa radin kansu, hakan ya faru ne sakamakon irin nasarar da aka samu a tattaunawar sulhu da aka bullo da shi a kasar.

Tun a watan Disambar 2013 ne, rikici ya auku a Juba babban birnin Sudan ta kudun, sama da al'ummar kasar miliyan biyu ne rikicin ya daidaita su inda suka tsere makwabtan kasashe domin neman mafaka.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China