in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangaren soja na Iran: Iran za ta janye daga yarjejeniyar batun nukiliya na Iran idan Amurka ta sake saka mata takunkumi
2017-10-31 13:35:29 cri
Hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Mohammad-Hossein Baqeri, ya bayyana a jiya Litinin cewa, Iran za ta janye daga yarjejeniyar batun nukiliyar ta, muddin Amurka ta sake saka mata takunkumi.

Jaridar Tehran Times ta kasar Iran ta ruwaito, Bageri ya bayyana hakan ne, yayin da ya halarci wani taron dakarun soja a wannan rana cewa, yana mai cewa dalilin daddale yarjejeniyar batun nukiliyar kasar Iran shi ne a soke takunkumin da kasashen yammacin duniya suka sakawa kasar ta Iran. Don haka idan har aka mayar da takunkumin, ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar ba shi da wata sauran ma'ana.

Bageri ya jaddada cewa, kasar Iran ta yi alkawarin bin yarjejeniyar batun nukiliya ta, amma idan kasar Amurka ta sake saka mata takunkumi, Iran din za ta janye daga yarjejeniyar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China