in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin kasar Rasha ta bukaci a mutunta yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran
2017-10-26 11:05:48 cri
Majalisar koli ta kasar Rasha ko kuma babbar majalisar dokokin kasar, ta bukaci a mutunta batun yarjejeniyar da aka cimma game da batun yin amfani da makamashin nukiliya a kasar Iran, a daidai lokacin da shugaban Amurka Donald Trump yayi barazanar yin watsi da yarjejeniyar.

A wata sanarwar data fitar, majalsiaar kolin kasar Rashar ta bukaci mambobin majalisar dokokin Amurka dasu gaggauta yin duk abin da ya dace domin shawo kan duk wata matsala da ka iya jefa batun cikin matsanancin hali.

Majalisar ta kuma bukaci majalisun dokokin kasashen Jamus, Faransa, China, Birtaniya da kungiyar tarayyar Turai, da su yi amfani da dukkan matsayin da suke da shi ta hanyar daukar matakan siyasa domin ganin an kiyaye yarjejeniyar da aka cimma mai cike da tarihi.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China