in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU, da Amurka za su hada gwiwa don yakar tsattsauran ra'ayi a Afrika
2017-10-26 10:47:58 cri
Kasar Amurka da kungiyar tarayyar Afrika (AU) sun sha alwashin yin hadin gwiwa domin yakar tsattsauran ra'ayi a nahiyar Afrika.

A ranar Laraba ne tawagar kiyaye zaman lafiya ta Amurka dake kungiyar tarayyar Afrika da kuma AU suka kaddamar da wani taron kwanaki 3 mai taken kawar da tashin hankali na masu tsattsauran ra'ayi (CVE) a helkwatar kungiyar tarayyar Afrika dake Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha.

Jessica Davis Ba, mataimakiyar babban jami'in shirin wanzar da zaman lafiya na Amurka a AU, ta yi alkawarin cewa, Amurkar za ta hada gwiwa da AU domin kawo karshen aukuwar munanan al'amurra makamancin wanda ya faru a Mogadishu ko kuma kamar harin da aka kaddamar a kasar Masar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China