in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU na goyon bayan a shiga tattaunawa domin warware rikicin yankin Gulf
2017-09-17 13:44:27 cri
Tarayyar Afrika ta jadadda bukatar warware rikicin yankin gulf bisa shiga tattaunawa da amfani da matakan diflomasiyya.

Kamfanin dillancin labarai na kasar Qatar ya ruwaito shugaban hukumar kula da ayyukan AU Moussa Faki Mohammed, na bayyana matsayin Tarayyar dangane da rikicin, inda ya yi kira da a warware shi ta hanyar hawa teburin sulhu da matakan diflomasiyya.

Mataimakin Firaministan Qatar kuma Ministan kula da harkokin Gwamnatin Kasar Ahmed bin Abdullah bin Zaid Al Mahmud, ya yi wa shugaban na hukumar AU bayyani dangane da halin da rikicin ke ciki, ranar Juma'a da ta gabata a birnin Addis Ababa na Ethiopia.

Ya kuma mika godiyar kasarsa game da matsayin da AU ta dauka dangane da batun warware rikicin ta hanyar shiga tattaunawa mai ma'ana tsakanin bangarorin dake rikici, tare da goyon bayan da ta nuna ga yunkurin shiga tsakani da Sarkin Kuwait Sheikh Sabah al-Ahmad al-Jaber ke jagoranta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China