in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF : idan ba a dauki matakin gaggawa ba, za a dauki sama da shekaru dari kafin kawo karshen auren wuri a yankunan yammaci da tsakiyar Afrika
2017-10-24 11:05:33 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya ce a yadda ake samun raguwar auren wuri a yanzu, za a dauki sama da shekaru 100 kafin kawo karshen matsalar.

Sabon hasashen da aka fitar yayin wani taron tattaunawa kan kawo karshen auren wuri da ya gudana jiya Litinin a Dakar babban birnin Senegal, na da nufin fiddo da yankunan da 'yan mata suka fi fuskantar barazanar auren wuri a duniya.

A cewar UNICEF, yayin da yawan auren wuri a yankunan yammaci da tsakiyar Afrika ya ragu cikin shekaru 20 da suka gabata, har yanzu da sauran rina a kaba, domin a cikin kowanne mata 10, akan yi wa hudu aure kafin su cika shekaru 18, sannan akan yi wa 1 daga cikin 3 aure kafin ta kai shekaru 15.

Yammaci da tsakiyar Afrika sun kushi kasashe 6 daga cikin 10 da aka fi samun yawan auren wuri a duniya, inda suka hada da Niger da Jamhuriyar Afrika ta tsakiya da Chadi da Mali da Burkina Faso da Guinea.

A cewar Bankin Duniya, dabi'ar na bukatar yunkurin kasashen duniya wajen rage talauci da karuwar jama'a, al'amarin dake da mummunan tasiri kan ci gaban ilimi da lafiyar mata da yara. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China