in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasa da kasa sun nuna yabo ga kokarin kafa tsarin buri daya na dan Adam da Sin take yi karkashin jagorancin jam'iyyar Kwaminis ta Sin
2017-10-22 13:22:10 cri
A cikin rahoton da babban satakaren jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, ya yi kira ga jama'ar kasa da kasa da su yi kokari tare don kafa tsarin buri daya na dan Adam, da kafa duniya mai zaman lafiya da tsaro da wadata da bude kofa da tsabta a dogon lokaci. A ganin kasa da kasa, kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan bin hanyar zaman lafiya da samun bunkasuwa a karkashin jagorancin jam'iyyar Kwaminis ta Sin, da sa kaimi ga kafa tsarin buri daya na dan Adam, da samar da tabbaci ga yanayin duniya, da samar da kuzari ga yunkurin neman kyakkyawar makomar dan Adam, da samar da gudummawa wajen yin kwaskwarima kan tsarin sarrafa duniya bisa fasahohin kasar Sin.

Mataimakin kwamitin jam'iyyar dake kan karagar mulkin kasar Rasha, wato jam'iyyar dinkuwar kasar Rasha Sergei Zheleznyak ya bayyana cewa, jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana kokarin kafa tsarin buri daya na dan Adam, da gabatar da shawarar "ziri daya da hanya daya", da sa kaimi ga yin mu'amala a tsakanin kasa da kasa a fannonin tattalin arziki da al'adu, da kirkire-kirkire da tsaro da sauransu. a halin yanzu, kasar Sin tana kokarin tabbatar da shimfida zaman lafiya a duniya da yankuna, da kasancewa muhimmiyar abokiya ga kasashen duniya da dama.

Mujallar The Atlantic ta kasar Amurka ta bayar da sharhi mai taken "Sin tana kokarin sake gina duniya" cewa, shawarar "ziri daya da hanya daya" muhimmiyar shawara ce dake shafar kasashen duniya da jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta gabatar. Bisa tsarin "ziri daya da hanya daya", cinikayyar dake tsakanin kasa da kasa zata taimaka wajen rage rikicin dake tsakanin kasa da kasa. Sharhin yace, kasar Sin tana kokarin taimakawa tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Manazarcin cibiyar nazarin manufofin diplomasiyya ta kasar Habasha Abebe Ehnert, ya bayyana cewa, Sin da Afirka suna da buri daya, manufofin da kasar Sin ta gudanar ga kasashen Afirka suna biyan bukatun bunkasuwar kasashen Afirka. Kasar Sin ta dauki alhakinta dake bisa wuyanta yadda ya kamata, kana ita ce kyakkyawar abokiyar kasashen Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China