in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sanarwa: CRI zai watsa labari kai tsaye kan bikin bude babban taron wakilan JKS
2017-10-16 16:49:01 cri
A ranar 18 ga watan nan da muke ciki da misalin karfe 9 na safe agogon Beijing, za a yi bikin bude babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19 a babban dakin taron jama'a dake birnin Beijing.

A daidai wannan lokaci, gidan rediyon kasar Sin wato CRI zai yi amfani da harsunan Sinanci da Ingilishi da na Rasha don watsa labaran bikin kai tsaye ta rediyo, da wasu shafukan intanet na CRI, ciki har da chinaplus.cri.cn, da kuma manhajar ChinaRadio da dai sauransu.

Baya ga haka, za a watsa labaran bikin kai tsaye ta wasu manhajoji na ChinaNews da ChinaTV da dai sauransu, har ma da dandalin sada zumunta na gida da na waje, kamar Facebook da Twitter da Weibo da kuma WeChat, cikin harsuna 40 da suka hada da Hausa da Sinanci da Ingilishi da Faransanci da dai sauransu, (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China