in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin sun fara taruwa a birnin Beijing
2017-10-16 10:31:55 cri
Za a bude babban taron wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 19 a ranar 18 ga watan nan da muke ciki. A sabili da haka, tun daga jiya Lahadi, wakilan jam'iyyar fiye da 2200 da za su halarci muhimmin taron, suka fara isowa birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, ta hanyoyin sufuri daban daban, inda za su wakilci daukacin 'yayan jam'iyyar fiye da miliyan 89.

Kafin isowar su Beijing, wakilan na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin sun shiga wurare daban-daban na kasar don gudanar da bincike, inda suka saurari ra'ayoyi da shawarwarin 'yan jam'iyyar da na jama'a, domin gabatar da su ga taron da zai gudana.

A ganin wadannan wakilan, kasar Sin tana cikin wani lokaci mai muhimmanci, inda take kokarin gina wata al'umma mai walwala da neman cika burinta na raya kasa da kyautata zaman rayuwar jama'a. Saboda haka, wannan muhimmin taro da za a kira zai taimakawa jama'ar kasar Sin a kokarinsu na raya kasa.

Rahotanni sun ce, ya zuwa karfe 8 da daren jiya Lahadi agogon Beijing, tawagogin wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin fiye da 10 ne sun iso birnin.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China