in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Faransa: Za a kori 'yan kasashen waje da suka aikata laifi
2017-10-16 13:23:11 cri
A jiya Lahadi ne agogon kasar Faransa shugaban kasar ta Faransa Emmanuel Macron ya halarci wani shirin telabijin a karon farko a matsayinsa na shugaban kasa, inda ya ce kasarsa za ta kori dukkan 'yan kasashen waje da suka yada zango a kasar ba bisa doka ba, gami da aikata laifi, a wani mataki na kara karfin kasar na yaki da ta'addanci.

A cewar shugaban, gwamnatin za ta yi kokarin kare jama'a, sai dai yana bukatar dukkan jama'ar kasar da su tsaya kan bakarsu don tinkarar abkuwar harin ta'addanci. Ya ce a ko da yaushe, a kuma ko'ina ne za a iya kai hari.

Ban da haka shugaban ya ce, duk da cewa bai yarda da wasu kudurorin da shugaban kasar Amurka Donal Trump ya tsayar dangane da tinkarar matsalar sauyin yanayin duniya, da yarjejeniyar da ta shafi batun nukiliya na kasar Iran ba, amma kasashen Faransa da Amurka kawaye ne, kuma za su ci gaba da yaki da ta'addanci kafada da kafada.

Yayin da yake magana kan batutuwan tattalin arziki da gyaran fuska game da tsarin zaman al'umma, wandada ke janyo hankalin jama'ar kasar Faransa, shugaba Macron ya ce, jerin matakan da ya dauka tare da zummar samar da guraben ayyukan yi, da raya tattalin arziki, za su fara haifar da sakamako cikin shekaru daya da rabi zuwa shekaru 2 masu zuwa. Ya ce a shirye yake ya gudanar da gyare-gyare a kasar.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China