in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasa rayuka sakamakon harin bom a Mogadishu ya kai 276
2017-10-16 12:57:57 cri
Hukumomin Somalia sun ce, harin bam da aka kai cikin wata mota a tsakiyar birnin Mogadishu ranar Asabar da ta gabata, ya haddasa mutuwar a kalla mutane 276 tare da raunata kimanin wasu 300.

Rahotanni sun ce, an samu jimilar ne bisa adadin da asibitoci daban-daban masu karbar wadanda harin ya rutsa da su suka bayar, inda kuma ake tsammanin yawan mutanen da suka rasa rayukansu ka iya karuwa.

A yammacin ranar Asabar da ta gabata bisa agogon kasar ne wata mota dauke da bom ta fashe a wajen wata mararrabar hanyoyi dake tsakiyar birnin Mogadishu, inda ke da yawan shaguna da otel da kuma gine-ginen gwamnati.

A daren ranar ne kuma shugaban kasar Mohammed Abdullahi Mohanmmed, ya kaddamar da zaman makoki na kwanaki 3, inda za a saukar da tutoci zuwa rabin sanda a wurare daban daban na kasar.

Zuwa yanzu babu wanda ya dauki alhakin harin. Amma a cewar kafofin watsa labarun kasar, watakila kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta Al-Shabaab ce ke da hannu a cikin lamarin. Kana mai yiwuwa ne, an so kai harin ga otel na Safari, inda aka fi samun yawan jami'an gwamnati da manema labaru da dai sauransu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China