in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matuka jirgin WFP sun tsallake rijiya da baya yayin da jirgin saman ya fadi a Somalia
2017-06-04 12:22:56 cri
Wani jirgin sama da hukumar samar da abinci ta MDD (WFP) ta yi hayarsa, ya gamu da matsala sa'an nan ya fadi a garin Garbaherey dake yankin Gedo a kudancin Somalia a ranar Asabar, inji jami'ar MDD.

Mai Magana da yawun hukumar ta WFP Amor Almagro, ta ce, karamin jirgin saman daukar kayan yayi saukar gaggawa ne dauke da matukansa 4 wadanda babu wata matsala data same su kuma dukkansu suna cikin koshin lafiya.

Almagro ta tabbatar da cewa jirgin saman daukar kayan mai matsakaicin girma wanda hukumar WFP ta dauki shatarsa, ya gamu da matsala a lokacin da yake kokarin sauka da sanyin safiyar ranar Asabar a Garbaharey dake kudancin Somalia.

Ta kara da cewa matukan jirgin su hudu dukkanninsu babu wata matsala data samesu kuma suna cikin koshin lafiya. Sai dai a cewarta jirgin ya samu mummunar illa.

Jami'ar MDD tace, kawo yanzu ba za'a iya bayyana takamamman dalilin da ya haddasa faruwar lamarin ba, sai dai za'a gudanar da bincike na hadin gwiwa tsakanin matuka jirgin da kuma hukumomin da abin ya shafa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China