in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Daliban Somalia sun samu tallafi karo karatu a Kasar Sin.
2017-09-07 11:01:24 cri
Daliban kasar Somalia 42 da suka fito daga bangarori daban-daban na kasar, sun samu tallafin karo karatu a jami'o'i daban-daban na kasar Sin.

Jakadan Kasar Sin a Somalia Qin Jian, ya ce daliban da suka kammala karatun sakandare za su ci gaba karatu a kasar Sin, inda ake sa ran za su koma su yi amfani da iliminsu wajen gina kasarsu.

Qin Jiang ya ce tallafin wani bangare ne na kudurin kasar Sin na taimakawa wajen farfado da kasar dake kahon Afrika tare da zurfafa huldar dake tsakaninsu.

A nasa bangaren, Ministan kula da ilimin gaba da sakandare na Somalia Abdirahman Dahir Osman, ya bayyana tallafin a matsayin babban ci gaba ga taimakon da kasar Sin ke ba kasarsa, inda ya ce ya na da muhimmanci wajen kara dankon dangantaka dake tsakanin kasashen biyu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China