in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
FAO: kasashe masu tasowa za su iya samun babban ci gaba a yankunan karkara
2017-10-13 10:35:53 cri
Hukumar kula da samar da abinci da aikin gona ta MDD(FAO) ta ce cikin shekaru gomai masu zuwa, miliyoyin matasan da ke kauyukan kasashe masu tasowa za su fara aiki, ta yadda za su taka muhimmiyar rawa ta fuskar raya yankunansu.

Hukumar ta bayyana haka ne cikin wani rahoto da ta fitar a baya-bayan nan kan yanayin da ake ciki wajen samar da abinci da kula da aikin gona a fadin duniya a bana.

Rahoton ya ce idan kasashe masu tasowa za su iya daidaita ayyukan samar da abinci da sauran sana'o'i masu alaka da shi a yankunan karkara, to akwai yiwuwar su samu damar raya tattalin arzikin yankunansu yadda ya kamata. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China