in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi hadin gwiwar tinkarar matsalar samar da isasshen abinci da zaman lafiya
2016-05-12 14:11:29 cri
Babban direktan hukumar kula da abinci da aikin gona ta M.D.D. (FAO) José Graziano da Silva, da wasu mutum 4 da suka samu lambobin yabo na Nobel, sun kaddamar da kawancen samar da isashen abinci da zaman lafiya a tsakanin hukumar FAO da masu lambobin yabo na Nobel.

An dai gudanar da taron ne a jiya Laraba 11 ga wata a birnin Rome da ke kasar Italiya. Yayin zaman, Da Silva ya ce, kawar da yunwa da talauci a duniya, ya zama babbar gudummawa ta samar da dauwamammen zaman lafiya. A sa'i daya kuma, aikin gona da samar da isasshen abinci, zai taimaka wa iyalai da yankunan da rikici ya shafa. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China