in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manoman kasar Sin sun samu karin kudin shiga
2017-09-30 12:47:27 cri
Han Changfu, Ministan aikin Noma na kasar Sin, ya ce kudin shiga da manoman kasar ke samu ya karu sosai cikin shekaru 5 da suka gabata.

Ministan wanda ya bayyana haka a jiya Juma'a yayin wani taron manema labaru, ya ce tallafawa manoma samun karin kudi shiga shi ne babban aikin hukumar, inda ya ce alkaluman da aka samu cikin wadannan shekaru 5 sun nuna cewa, hakar ta cimma ruwa.

A cewar jami'in, kudin shiga da manoman kasar Sin suke samu ya karu da kashi 47.4% a cikin shekaru 4 da suka gabata. Kuma an fi samun karuwar kudin shigar ne a yankunan dake fama da talauci, inda yake karuwa da kashi 10% a kowace shekara.

Ministan ya kara da cewa, ta wanna hanya, kasar Sin ta samu damar rage adadin al'ummarta dake fama da talauci, da kusan miliyan 13 a kowace shekara, ya na mai alakanta wannan ci gaba, da kokarin gwamnatin kasar na rage gibin dake tsakanin birane da yankunan karkara. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China