in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF: Yara 450,000 na fuskantar barazanar rashin abinci mai gina jiki a arewa maso gabashin Najeriya
2017-09-29 21:06:41 cri
Asusun kula da kananan yara na MDD UNICEF, ya ce akwai yara kanana da yawan su ya doshi 450,000 dake fuskantar barazanar rashin samun abinci mai gina jiki a arewa maso gabashin Najeriya. Hakan a cewar asusun ya biyo bayan tashe tashen hankula da suka addabi yankin cikin kusan shekaru 8, sakamakon tarzomar Boko Haram.

Da yake tabbatar da hakan a Juma'ar nan, mataimaki daraktan asusun na UNICEF Justin Forsythe, wanda ya gudanar da ziyarar aiki ta kwanaki 3 a yankin, ciki hadda birnin Maiduguri fadar mulkin jihar Borno, ya shaidawa manema labarai cewa, akwai yara kanana kusan miliyan daya da suka rasa matsugunnan su, ciki hadda yaran da shekarun su ba su wuce 5 ba, su kusan 450,000 da ake tsoron na iya rasa damar samun abinci mai gina jiki a yankin.

Kaza lika jami'in na UNICEF ya ce, bisa kiyasi akwai yara kanana miliyan 3 wadanda rikicin Boko Haram ya raba da makarantun su, a yankin na arewa maso gabashin Najeriya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China