in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabon shugaban babban taron MDD yana fatan kasar Sin za taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa
2017-09-13 09:57:43 cri
Sabon shugaban babban zauren MDD Miroslav Lajcak, ya bayyana fatan cewa, kasar Sin za ta kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa.

Mr Lajcak wanda ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai bayan bude zaman babban zauren majalisar karo na 72, ya ce yana farin cikin ganin yadda kasar Sin take ci gaba da taka wannan rawa da yadda take magana ba wai a matsayinta na kasa ba, amma a matsayinta na mai yayata manufofin MDD.

Ya kuma yi alkawarin cewa, zai yi aiki da dukkan kasashe mambobin majalisar, ta hanyar tuntubar juna don ganin an cimma nasarar manufofin da aka sanya a gaba. Kana ya ce, kofarsa a bude take ga kowa don karbar shawarwari masu ma'ana.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China