in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar G 77 da Sin sun yi kiran da a rika sauraran kasashe masu tasowa
2015-09-25 09:54:21 cri
Shugabar kungiyar G 77 da kasar Sin sun yi kira ga masu shiga tsakanin a kasashen duniya, da su rika baiwa kasashe masu tasowa damar bayyana ra'ayoyinsu a batutuwan tafiyar da harkokin da suka shafi duniya.

Shugabar kungiyar Nkoana-Mashabane kana ministar kula da harkokin kasa da kasa ta kasar Afirka ta kudu ta bayyana hakan ne kwana guda gabani ganawar da shugabannin kasashen duniya za su yi don cimma daidaito kan manufofin samun dauwamammen ci gaba na MDD.

Ta ce, kungiyar kasashen na G 77 da Sin suna taka muhimmiyar rawa wajen tsara ajandodin da suka shafi ci gaba mai dorewa da kuma sauyin yanayi, kuma za su ci gaba da yin hakan a madadin al'ummomin da aka mayar da su saniyar ware a duniya.

Madam Nkoana-mashabane ta ce, baiwa kungiyar ta G 77 irin wannan dama zai taimaka musu matuka ganin cewa, su ne ke da kasashe da dama a sassa daban-daban na duniya.

Ta kuma yi maraba da abubuwan da ke kunshe cikin ajandar samun bunkasuwa bayan shekara 2015, wadda ake saran shugabannin kasashen duniya za su amince da ita yayin taronsu a yau Jumma'a.

Ita dai wannan ajanda tana bayani ne kan nauyin da ke kan kasashe masu sukuni da marasa karfi wajen magance matsaloli kamar matsalar canjin yanayi da rashin daidaito da ake fuskanta a duniya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China