Daukacin mambobin majalisar ne suka amince da kudurin mai lamba 2376, wanda ya tsawaita ayyukan shirin, tare da mara baya ga tsarin siyasar da ke kunshe cikin yarjejeniyar siyasar kasar da aka cimma.
Manyan ayyukan shirin sun hada da mara baya ga muhimman cibiyoyin kasar da samar da ayyukan jin kai idan ana bukata tare da sa ido kan hakkokin dan Adam da bada rahoto.
Sauran sun hada da kawar da makamai da sauran abubuwa dake da alaka da yaki da yaduwar makamai da kuma taimakawa gwamnatin kasar a kokarin da take na farfado da yankunan da rikici ya rutsa da su, ciki har da wadanda aka 'yanto daga hannun kungiyar IS. (Fa'iza Mustapha)