in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya shugabanci shawarwarin siyasa na 4 a yayin babban taron MDD na 4 a tsakanin ministocin harkokin wajen Sin da Afirka
2017-09-21 14:55:08 cri
A jiya ranar 20 ga wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwararsa ta kasar Afirka ta Kudu madam Maite Nkoana-Mashabane sun shugabanci shawarwarin siyasa na 4 a yayin babban taron MDD a tsakanin ministocin harkokin wajen kasar Sin da kasashen Afirka a cibiyar MDD dake birnin New York, inda ministoci da wakilai kimanin 50 suka halarci shawarwarin.

Wang Yi ya bayyana cewa, Sin da kasashen Afirka sun kasance abokai masu buri iri daya da yin hadin gwiwar samun moriyar juna. Kamata ya yi kasar Sin da kasashen Afirka su kara hadin gwiwa da juna, da yin amfani da fifikonsu wajen raya kansu da hadin gwiwar Sin da Afirka, da canja damar hadin gwiwa zuwa sakamakon hadin gwiwa. Ya kamata a aiwatar da sakamakon taron koli na Johannesburg na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, da sa kaimi ga shirye-shiryen hadin gwiwa guda 10, da kara azama kan aiwatar da shawarar "ziri daya da hanya daya", ta haka kasashen Afirka za su ci gajiya sosai.

A cikin jawabinsu, ministocin harkokin wajen kasashen Afirka sun nuna godiya ga kasar Sin domin ta samar da gudummawa ga kasashen Afirka a dogon lokaci, da nuna goyon baya ga shawarar "ziri daya da hanya daya", da nuna yabo ga kasar Sin domin ta aiwatar da sakamakon taron koli na Johannesburg na dandalin tattaunawar, kuma suna fatan bangarorin biyu za su zurfafa hadin gwiwarsu a dukkan fannoni, da samun moriyar juna da bunkasuwa mai dorewa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China