in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ecuador na iya samun gurbin buga kasar cin kofin duniya in ji kocin ta
2017-09-21 09:28:09 cri
Sabon kocin kungiyar kwallon kafar kasar Ecuador Jorge Celico, ya ce har yanzu yana da kwarin gwiwar cewa, kungiyar da yake horaswa za ta kai ga samun gurbi, na buga gasar cin kofin duniya da hukumar FIFA ke shiryawa.

Jorge Celico ya bayyana hakan ne, bayan da suka buga wasanin su na rukuni da tarin kalubale. Yanzu haka dai kungiyar ta Ecuador ita ce ta 8 a rukunin kungiyoyin kasashen kudancin Amuka ko CONMEBOL, kuma ya zamewa kungiyar wajibi ta lashe wasannin ta na neman gurbin guda 2, na daya da kungiyar kasar Chile a ranar 5 ga watan Oktoba, dayan kuma a gida da Argentina kwanaki 5 bayan wasan na farko.

Koci Celico ya ce yana da 'yan wasa masu kwazo, abun da kawai suke bukata shi ne hada karfi wuri guda, domin ganin sun lashe wasannin 2 na gaba.

Ecuador dai ta sallami tsohon kocin ta Gustavo Quintero. Koci Celico ya kuma ce bai gamsu da uzurin da tsohon kocin kungiyar Quintero ba, na cewa 'yan wasan sa sun gaza cimma nasarar wasannin su na baya ne, sakamakon tudun filin wasan da suka taka leda a cikin sa a birnin Quito.

An ce filin wasan ya kai tudun mita 2,700 daga doron kasa. Ya ce duk da hakan ba zai hana 'yan wasan samun nasara ba.

Kungiyoyi 4 dake rukunin mafiya hazaka ne dai zasu wakilci rukunin, a gasar cin kofin duniyar da za ta gudana badi a kasar Rasha, yayin da ta 5 za ta kara da wata kungiyar wajen nahiyar domin samun gurbi.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China