in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Birtaniya sun kama wani da ake zargi da hannu cikin harin bom na birnin London
2017-09-17 12:57:43 cri
'Yan Sandan Birtaniya sun kama wani da ake zargi da hannu wajen kai harin bom a tashar jirgin karkashin kasa na birnin London a ranar Juma'a. An kama mutumin ne jiya a birnin Dover dake kudu maso gabashin kasar, a dab da bakin teku.

Cikin wata sanarwa da 'yan sandan suka fitar a jiya, sun ce an kama mutumin mai shekaru 18 a duniya bisa zargin aikata ayyukan ta'addanci.

A nasa bangaren, babban jami'in 'yan sandan birnin London, ya ce aikin da aka gudanar na cafke mutumin na da muhimmanci matuka, sannan za a kiyaye matsayin koli na barazanar harin ta'addancin da kasar ke fuskanta, wato mataki mafi hadari.

A ranar Jumma'a da ta gabata ne, aka samu fashewar bom a wata tashar jirgin karkashin kasa a yammacin birnin London, lamarin da ya haddasa jikkatar mutane kimanin 30.

Daga bisani dai, kungiyar IS mai kaifin kishin Islama ta sanar da daukar nauyin harin.

Zuwa daren Jumma'ar ne kuma, firaministar Birtaniya Teresa May ta sanar da daga matsayin barazanar ta'addancin da kasar ke fuskanta, daga matsayi 'mai tsanani' zuwa 'mafi hadari'.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China