in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta karbi bakuncin taron hadin gwiwa na duniya kan yaki da cin hanci da rashawa
2017-09-16 12:48:56 cri
Hukumar yaki da cin hanci ta kasar Sin da hadin gwiwar Bankin Duniya, za su karbi bakuncin taron hadin gwiwa na kasa da kasa kan yaki da cin hanci da rashawa daga ranar 19 ga wata a nan birnin Beijing.

Taron na yini biyu, zai mai da hankali ne kan batutuwan da suka hada da rawar da gwamnati za ta iya takawa wajen samar da kyakkyawan yanayin kasuwanci da tsaftace harkokin kasuwanci da kuma hadin gwiwa wajen yaki da cin hanci tsakanin kasashen dake cikin shawarar "Ziri daya da hanya daya"

Shawarar "Ziri daya da hanya daya" da kasar Sin ta gabatar a shekarar 2013, na da nufin sake gina hanyar tattalin arziki ta siliki da kuma hanyar Siliki ta cikin ruwa ta karni na 21, bisa hadin gwiwa tsakanin kasashen da ke cikin shawarar domin moriyarsu baki daya, ta hanyar inganta cinikayya ba tare da wani tarnaki ba da kawance a fannin harkokin kudi da samar da kayayyakin more rayuwa da mu'amala ta kut-da-kut tsakanin al'ummominsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China