in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin ta'addanci ya jikkata wasu a London
2017-09-15 19:46:04 cri

Da safiyar yau Jumma'a ne wasu ababen fashewa suka tashi, a wata tashar jirgin karkashin kasa dake yammacin birnin London na kasar Ingila, lamarin da ya sabbaba jikkatar wasu mutane. 'Yan sandan wurin sun sanar da cewa, kwarya-kwaryar sakamakon bincikensu ya shaida cewa, 'yan ta'adda ne suka kitsa lamarin.

A dai yau din, kakakin firaministar Ingila ya cewa, madam Theresa May ta maida hankali matuka game da aukuwar harin, tana kuma tuntubar sassa masu ruwa da tsaki, domin kara fahimtar abun da ya faru a kan lokaci. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China