in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an Afrika sun jinjinawa kotuna al'umma bisa saukaka hanyoyin samun shari'a
2017-08-23 09:51:18 cri
Masana harkokin shari'a dake taro a Kigali babban birnin Rwanda, sun yi kira da hade tsare-tsaren shari'o'in zamani da na al'umma domin saukaka samun shari'a a Afrika.

Babban Jojin Sierra Leone Abdulai Hamid Charm, ya ce suna sane da muhimmancin cibiyoyin shari'a wajen inganta bada dama ga samun shari'a, amma kuma sun lura da iyakar da suke da ita.

Ya ce akwai bukatar masana harkokin shari'a, su hada hannu da cibiyoyin shari'a na al'umma domin bada dama ga wadanda ke matukar bukatar ayyukansu.

Abdulai Hamid Charm, na wannan jawabi ne yayin bude taron yini uku na nahiyar game da hadin gwiwa tsakanin bangaren shari'a da cibiyoyin shari'a na al'umma dake gudana a Kigali.

Taron ya samu mahalarta daga sama da kasashe 15 na fadin nahiyar, domin tattauna hanyoyin karfafa hadin gwiwa tsakanin bangaren shari'a da cibiyoyin shari'a na al'umma. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China