in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yang Jiechi ya gana da sakataren harkokin wajen kasar Amurka
2017-09-13 13:11:10 cri
Jiya ne memban majalisar gudanarwar kasar Sin Yang Jiechi ya gana da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Rex Tillerson a lokacin da ya yada zango a kasar Amurka bayan kammala ziyararsa a kasar Jamaica

A yayin ganawar, Yang Jiechi ya yi nuni da cewa, tabbatar da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ya dace da moriyar kasashen biyu, kuma shi ne burin kasashen duniya.

A cewar Yang, a bana ne ake sa ran shugaban kasar Amurka Donald Trump zai kawo ziyara kasar Sin bisa gayyatar takwaransa na kasar Sin Xi Jinping. kasar Sin tana fatan hada kai tare da kasar Amurka don ganin ganawar ta yi nasara.

A nasa bangare, Tillerson ya bayyana cewa, shugaba Trump yana begen ziyarar da zai kai kasar Sin a bana, yana kuma son tsara makomar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka tare da shugaban kasar Sin Xi Jinping. Kasar Amurka tana fatan hada kai tare da kasar Sin a fannin musayar ra'ayi a fannin zamantakewar al'umma, da al'adu, a tsakanin kasashen biyu zagaye na farko, da tattaunawa kan dokoki da tsaron yanar gizo, da zurfafa hadin gwiwa a dukkan fannoni, da kara yin mu'amala da juna kan manyan batutuwan duniya da yankuna, bisa tushen musayar ra'ayi a fannonin harkokin waje da tattalin arziki a tsakaninsu. Ana fatan sakamakon da za a samu a yayin ganawar shugaba Trump da shugaba Xi a kasar Sin za ta sa kaimi ga samun bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China