in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta kudu za ta karbi bakuncin taron yawan al'umma na kasa da kasa
2017-09-13 10:06:26 cri
Yanzu haka ta tabbata cewa, kasar Afirka ta kudu ce za ta karbi bakuncin taron yawan al'umma na kasa da kasa,domin zakulo hanyoyin magance matsalolin da suka shafi yawan al'umma da ke addabar duniya.

Taron wanda zai gudana daga ranar 29 ga watan Oktoba zuwa 4 ga watan Nuwamban wannan shekara, zai kuma taimaka wajen magance matsalar talauci da jahilci ko rashin karatu da rubutu a wuraren da ake samun karuwar yawan al'umma.

Babban jami'in kididdiga a hukumar kididdigar kasar Pali Lehohla, ya ce taron zai kuma kara samar da damammaki ga zuriyar da ke tafe a fannonin da ake da matsala a halin yanzu, da yiwa gwamnati jagora kan yadda za ta sake bibiyar manufofinta na yawan al'umma.

Kimanin masana 2,000 a wannan fanni da masu tsara manufofi, kungiyoyin fararen hula da shugabannin gwamnati daga kasasahe 131 ne ake saran za su tattauna game da matsalar talauci a duniya, da mutuwar mata masu juna biyu,shekarun rayuwa a duniya. Sauran sun hada da cutar kanjamau, hanyoyin samun Ilimi da matsalar rashin ayyukan yi,da Ilimin jima'i da lafiyar kwakwalwa, da kalubalen da irin wadannan manufofi suke fuskanta a nahiyar Afirka da batun kaurar jama'a da sauran batutuwa da suka shafi yawan al'umma da na raya kasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China