in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a jefa kuri'u a rufe kan batun yanke kauna ga salon shugabancin Jacob Zuma
2017-08-08 12:22:21 cri
Shugabar majalisar dokokin jama'ar kasar Afirka ta Kudu Baleka Mbete, ta sanar a gun taron manema labaru da majalisar dokokin jama'ar kasar ta gudanar a jiya Litinin 7 ga watan nan cewa, za a jefa kuri'u a asirce, kan batun yanke kauna ga mulkin shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma.

Za a yi muhawara kan wannan batu ne a ranar 8 ga watan nan a majalisar dokokin kasar.

Bayan rusa majalisar dokokin kasar a karshen Maris na bana da shugaba Zuma ya yi, jam'iyyar adawa ta kasar ta sake gabatar da batun yanke kauna ga salon mulkin shugaba Zuma, tana mai bukatar a jefa kuri'u ba tare bayyana rajistar masu kuri'ar ba, don sa kaimi ga 'yan majalisar dokokin kasar daga jam'iyyar dake kan karagar mulki, wadanda suke tsoron abun da ka je ya zo idan har suka jefa kuri'un amincewa.

Bisa dokokin kasar, idan aka zartas da kuri'ar debe kauna ga shugaba Zuma, shugaban da dukkan majalisar ministocin gwamnatinsa za su yi murabus, kana Mbete za ta zama shugabar kasar ta wucin gadi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China