in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IAEA ta jinjinawa kokarin kasar Sin na kare makamashin nukiliya
2017-09-12 13:53:45 cri
Hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta jinjinawa kokarin kasar Sin da ci gaban da ta samu wajen inganta kare makamashin nukiliya da ba da gudumawa wajen tsaron makamashin a duniya.

Hukumar ta bayyana haka ne bayan ta kammala nazarin tsaron nukiliyar kasar Sin da ta yi a karon farko, bisa bukatar hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasar. IAEA ta kammala aikin nazarin da ya shafe kwanaki 10 ne a ranar Jumma'ar da ta gabata.

A rahotonta, hukumar ta ce kasar Sin ta dauki managartan matakan samar da ayarin tabbatar da tsaron nukiliyar da kiyaye dabarun tsaron, sannan ta taka muhimmiyar rawa wajen mara baya ga kawancen kare nukiliya a matakin yanki da ma duniya baki daya.

Shugaban sashen kula da kayayyaki da naurori na hukumar Muhammad Khaliq, ya ce yadda kasar Sin ke aiwatar da matakan kare makamashi da yadda take amfani da shawarwarin hukumar, alama ce dake nuna jajircewarta wajen tabbatar da tsaron nukiliya a ciki da wajen kasarta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China