in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Isra'ila ta jinkirta taron koli da za ta yi da kasashen Afirka
2017-09-12 10:20:10 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Isra'ila, ta ce bisa bukatar shugaban kasar Togo Faure Essozimna Gnassingbé, an dage taron koli da kasar za ta yi da kasashen Afirka, wanda a baya aka tsara gudanarwa daga ranar 23 zuwa 27 na watan Oktoba a birnin Lome na kasar Togo.

Sanarwar da ma'akatar ta fitar a jiya, ta yi nuni da cewa, domin tabbatar da gudanar taron cikin nasara, kasar Togo tana bukatar gudanar da karin shirye-shirye. Sai dai kuma, sanarwar ba ta bayyana yaushe za a gudanar da taron ba.

Jaridar The Time of Israel ta ruwaito cewa, watakila za a soke gudanar da taron, la'akari da kin amincewa da shi da kasar Palesdinu da wasu kasashen Afirka su ka yi.

Don kyautata dangantakar dake tsakanin Isra'ila da kasashen Afirka, Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya taba kai ziyara kasashen Rwanda da Kenya da Uganda da Habasha da sauran wasu kasashen Afirka a shekarar 2016, kana ya halarci taron koli na kungiyar ECOWAS da aka gudanar a kasar Liberia a watan Yunin bana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China