in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Isra'ila sun kashe wasu mutane 4 dake dauke da makamai
2016-11-28 12:27:51 cri
Bangaren sojojin kasar Isra'ila ya sanar a Lahadi 27 ga wata da cewa, wasu sojojinsa sun yi musayar wuta da wasu mutanen dake dauke da makamai a kan iyakar Isra'ila da Sham, inda aka kashe masu dauke da makamai 4. A cewar sojojin Isra'ila, mutanen da suka mutu suna da alaka da kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta IS.

A safiyar Lahadi bisa agogon wurin, daga cikin yankin da kasar Sham ta mallaka kan tudun Golan, wasu dakaru sun kai hari ga yankin da sojojin Isra'ila suka mallaka, inda daga cikin makaman da suka yi amfani da su har da karamar igwa. Nan take sojojin Isra'ila sun mayar da martani, kuma sun tura jiragen saman yaki domin yin luguden boma-bomai. Sakamakon dauki-ba-dadi shi ne an lalata motoci da makamai na dakarun, tare da kashe wasu 4 daga cikinsu. Yayin da a bangaren sojojin Isra'ila, babu wanda ya mutu ko kuma ya ji rauni.

A cewar sojojin saman Isra'ila, mutanen 4 mambobi ne na kungiyar Yarmuk Martyrs, wadda ke da alaka da kungiyar IS.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China