in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin Syria sun kawar da kawanyar da kungiyar IS ta yi wa filin jirgin saman birnin Deir al-Zour
2017-09-10 13:24:41 cri
A jiya Asabar ne, sojojin gwamnatin kasar Syria suka yi nasara a fatatawar da suka yi da dakarun kungiyar IS a lardin Deir al-Zour dake gabashin kasar, inda suka kawar da kawanyar da kungiyar IS ta yi wa filin jirgin saman soja dake birnin Deir al-Zour, fadar mulkin lardin.

Wani jami'in gwamnatin kasar ya bayyana cewa, wannan shi ne babban ci gaba da aka samu a matakan soja da aka dauka a kan kungiyar IS, lamarin da zai kawo karshen kungiyar IS a lardin Deir al-Zour baki daya.

Rundunar sojan kasar Syria ta bayyana cewa, halin yanzu, sojojin gwamnatin kasar suna ci gaba da kai hare-hare kan kungiyar IS dake birnin Deir al-Zour ta hanyoyi guda biyu.

Lardin Deir al-Zour yana gabashin kasar Syria, muhimmin wurin da ake hako man fetur kasar Syria, kana ya yi iyaka da kasar Iraki. Tun a shekarar 2014 ne dai kungiyar IS ta ke rike da lardin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China