in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Syria ta yi kira ga MDD da a wargaza kawancen kasa da kasa da kasar Amurka ta jagoranta
2017-07-31 10:32:44 cri
A jiya ne ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta mikawa babban sakataren MDD da shugaban kwamitin sulhun majalisar wasika, inda ta yi kiran da wargaza kawancen kasa da kasa da kasar Amurka ta jagoranta biyo bayan zargin kawancen da kai hare-hare ta sama wadanda suka haddasa mutuwa da raunatar fararen hula.

A cikin wasikar, ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta bayyana cewa, tun da aka kafa wannan kawance zuwa wannan lokaci, ta kai hare-hare ta sama sau da dama. Ta ce, koda a watan Yulin bana, kawancen ya kai hare-hare ta sama sau 7 a jihar Deir ez-Zor dake gabashin kasar Syria da jihar Al Hasakah dake arewa maso gabashin kasar, wadanda suka haddasa mutuwa da raunatar fararen hula da dama, ciki har da mata da yara.

A watan Satumba na shekarar 2014 ma, kawancen kasa da kasa wanda kasar Amurka da sauran kasashe suka kafa ya kai hare-hare ta sama kan sansanonin kungiyar IS dake kasashen Syria da Iraki. A saboda haka gwamnatin kasar Syria na ganin cewa, kawancen da Amurkar ke jagoranta bai samu izinin kai irin wadannan hare-hare daga kwamitin sulhun MDD ba, wadanda suka haddasa mutuwa da raunatar fararen hula da dama. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China