in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta kakabawa wasu jami'ai a Sudan ta kudu takunkumi
2017-09-07 11:06:48 cri
A jiya Laraba ne kasar Amurka, ta kakabawa wasu jami'an kasar Sudan ta kudu su 2, da wani tsohon jami'in kasar daya, tare da wasu kamfanonin kasar 3 takunkumi. Amurka dai ta zargi sassan da aka sanyawa takunkumin da yiwa shirin wanzar da zaman lafiya a kasar kafar ungulu.

A cewar sashen dake lura da harkokin cikin gida da lalitar Amurka, takunkumin ya shafi mataimakin ministan tsaron kasar Malek Reuben, da ministan watsa labaran kasar Michael Makuei, da tsohon hafsan hafsoshin sojojin kasar Paul Malong.

Wata sanarwa da sashen lura da latitar Amurkan ya fitar ta bayyana cewa, kamfanoni 3 da lamarin ya shafa mallakar Mr. Reuben ne, kuma Amurka za ta ci gaba da jaddadawa jagororin Sudan ta kudu, wajibcin biyayya ga yarjejeniyar tsagaita wuta.

Kaza lika ya zama tilas a martaba yarjejeniyar shekarar 2015 da aka sabunta, wadda ta tanaji matakan warware takaddamar siyasa dake addabar Sudan ta kudu, ta hanyar tattaunawa mai ma'ana tare da tsagin 'yan adawar kasar. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China