in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin zai tattaunawa da jagororin hukummomin kudi na kasa da kasa
2017-09-06 18:55:58 cri
A ranar Talata mai zuwa ne, firaministan kasar Sin Li Keqiang zai tattaunawa da shugabannin hukumomin kudi da tattalin arziki na kasa da kasa guda shida a nan birnin Beijing,fadar mulkin kasar Sin.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai, ya ce, wadannan jagorori sun hada da shugaban bankin duniya Jim Yong Kim,babbar darektar asusun ba da lamuni na kasa da kasa Christine Lagarde, da babban darektan kungiyar cinikayya ta duniya Roberto Azevedo, da babban darektan kungiyar kwadago ta duniya Guy Ryder. Sauran sun hada da babban sakataren kungiyar tattalin arziki da raya kasashe Angel Gurria sai kuma shugaban hukumar daidaita harkokin kudi Mark Carney.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China