#BRICS# Xi Jinping: Ya kamata a yada nagartaccen ra'ayin tsaron duniya
Cikin jawabinsa, shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya ce kasashen BRICS suna kokarin kare zaman lafiya a duniya, da raya tsarin duniya ta fuskar tsaro. Ya kuma yi kira ga dukkanin kasashen BRICS da su martaba kundin tsarin mulkin MDD da manyan ka'idojin da ake bi wajen kula da harkar kasa da kasa, da tabbatar da ganin Karin kasashe sun shiga ana damawa da su wajen kula da harkokin duniya, da yaki da ra'ayin babakere da kashin dankali a duniya. Har ila yau, Ya bukaci a yi kokarin yayata wani nagartaccen tsarin a fannin tabbatar da tsaro, wanda zai kasance na bai daya tare da hadin gwiwa mai dorewa, ta yadda za a yi kokari wajen warware wasu batutuwan kasa da kasa dake jan hankalin al'ummar duniya.(Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku