in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kara nuna goyon baya ga kasashen Afirka don dakile kwararar 'yan gudun hijira da bakin haure
2017-08-29 10:37:38 cri
Jiya ne a birnin Paris na kasar Faransa, shugabannin kasashen Afirka da Turai suka gudanar da wani taron koli game da batun bakin haure, inda aka tsaida kudurin kara nuna goyon baya ga kasashen ta yadda za su canja alakar jiragen dake dauke da 'yan gudun hijira da yaki da bakin haure zuwa nahiyar turai.

Shugabannin kasashen Faransa, Jamus, Italiya, Spaniya, Chadi, Nijer, Libya da sauran kasashe da kuma wakilan kungiyar EU ne suka halarci taron. Bayan taron shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya bayyana wa manema labaru cewa, kamata ya yi bangarori daban daban ciki har da kasashen da 'yan gudun hijira suke fitowa da su canja alakar jirgen, kana su dauki matakai tare don tinkarar batun, wannan wani kalubale ne da kungiyar AU da EU ya kamata su fuskanta tare.

Rahotanni na cewa, a yayin taron, an tsai da kudurin kara nuna goyon baya ga Jamhuriyar Nijer da Chadi, da kara sa kaimi ga samar da zaman lafiya a fannin siyasa a kasar Libya. Haka kuma kasashen Faransa da Jamus da Italiya da kuma Spaniya sun yi alkawarin kara yin hadin gwiwar tattalin arziki don kyautata yanayin zaman rayuwar jama'a dake gudun hijira. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China