in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Nijeriya, za a rufe sansanonin 'yan gudun hijira dake Jihar Adamawa
2016-12-29 10:31:35 cri
Gwamnatin jihar Adamawa dake yankin Arewa maso Gasashin Nijeriya, a jiya Laraba, ta ce za ta rufe sansanonin 'yan gudun hijra dake fadin jihar a cikin watan Junairu mai kamawa.

Mataimakin Gwamnan jihar, Martin Babale ne ya bayyana haka, jiya Laraba a garin Yola babban birnin Jihar, lokacin da yake yi wa manema labarai bayani game da abubuwan da aka cimma a taron majalisar tsaro ta jihar

Ya ce gwamnati za ta dauki matakai da suka hada da karfafawa 'yan gudun hijirar komawa kauyukansu, tare da hada hannu da masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da daga nan zuwa ranar 30 ga watan Junairu, dukkan 'yan gudun hijirar sun bar sansanonin,.

Mataimakin Gwamnan ya ce, ci gaba da zaman 'yan gudun hijira a sansanonin bayan kwace iko da duka garuruwan da rikicin ya shafa, abu ne da zai rage darajar jihar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China