in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'ar MDD: Kasar Sin ta kasance jagora a fannin magance sauyin yanayi
2017-08-29 08:59:45 cri
Sakatariyar babban taro kan sauyin yanayi na MDD(UNFCCC) Patricia Espinosa ta yaba da matakan da mahukuntan kasar Sin ke dauka kan magance matsalar sauyin yanayi da duniya ke fuskanta.

Jami'ar wadda ta bayyana hakan yayin wata ziyarar kwanaki uku da ta kawo kasar Sin, ta kuma ce kasashe da dama na duniya sun rungumi wadannan matakai da kasar Sin ta yi amfani da su wajen tunkarar matsalar sauyin yanayi a kasashensu.

Wasu daga cikin wadannan matakai da kasar ta Sin ta yi amfani da su, a cewar Madam Patricia, sun hada da fasahohin zamani marasa gurbata muhalli baya ga wasu sabbin dabaru duk da nufin inganta rayuwar Sinawa.

Jami'ar ta kuma bayyana mahukuntan kasar Sin, a matsayin jagorar magance matsalar sauyin yanayi a duniya. Ta ce kasar Sin ta aiwatar da managartan matakan alkinta muhalli a zahiri, wadanda suka samu yabo daga MDD. Har ma sun kasance abin koyi ga sauran kasashen duniya.

Wannan dai ita ce ziyarar Madan Patricia Espinosa ta farko zuwa nan kasar Sin a matsayin jami'ar MDD mai kula da sauyin yanayi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China