in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Iran ya yi maraba da komawar jakadan Qatar
2017-08-25 11:07:30 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran ta nuna gamsuwa da aniyar gwamnatin Qatar, ta sake mayar da jakadan ta birnin Tehran, domin ci gaba da ayyukan diflomasiyya kamar yadda aka saba.

Wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar a jiya Alhamis, ta bayyana shirin ta na mayar da jakadanta kasar Iran, tare da burin sake bunkasa dangantakar sassan biyu a dukkanin fannoni. To sai dai sanarwar ba ta ayyana lokacin aiwatar da hakan ba.

A watan Janairun shekarar 2016 ne kasar Qatar ta janye jakadan ta daga Iran, bayan da Saudiyya ta yanke alaka da Iran din, bisa zargin mahukuntan kasar da gazawa wajen kare ofishin jakadancin ta dake birnin Tehran, da wani ofishin ta dake Mashahd, wanda hakan ya baiwa masu zanga zanga damar lalata ofisoshin.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China