in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin zirga-zirgar jiragen saman Saudiya bai samun izinin jigilar maniyata daga Katar ba
2017-08-21 14:11:08 cri
Kamfanin zirga-zirgar jiragen saman na kasar Saudiya ya sanar a jiya Lahadin cewa, har zuwa yanzu bai samu izini daga kasar Katar ba game da jigilar masu aikin hajji daga babban birnin kasar Doha ba.

Rahotanni na cewa, a kwanan baya ne wani dan gidan sarautar Katar ya gana da yarima mai jiran gado na kasar Saudiya Mohammed bin Salman Al Saud, inda ya bayyana fatansa na ganin kasar Saudiya ta baiwa 'yan Katar damar samun zuwa aiki Hajji a birnin Mekka. Daga baya kuma, sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud na Saudiya ya ba da umurnin sake bude kan iyakar kasashen biyu, wanda aka rufe sakamakon takun sakar diplomasiyya da Katar, kana ya ce zai biya kudin jigilar jiragen saman maniyatan kasar ta Katar. Ya zuwa yanzu an bude kan iyakar, kuma 'yan kasar Katar sama da 100 sun shiga kasar Saudiya ta mota don halartar aikin Hajjin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China